Labarin da muka samu daga shafin Leadership a yau ya shaida cewa, sama da mutane dubu 30 ne suka tsere daga mahaifarsu na garin Rann dake garin Maiduguri wacce take iyaka da kasar Kamaru. Majalisar dinkin duniya a yau Talata ta bayyana cewa; al'ummar sun arce ne a karshen makon nan saboda tsoron sabbin hare-haren Boko Haram.
"Dukkanin al'ummar ya nuna a firgice suke, suna ta ficewa ne domin tseratar da rayukansu." In ji Babar Baloch mai magana da yawun hukumar dake kula da 'yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya wanda ya shaidawa manema labarai a birnin Geneva.