Yau Talata da safe ne majalisar wakilan jama'ar kasar Sin NPC wato majalisar kafa dokokin kasar, ta bude taron shekara-shekara, inda Xi Jinping da sauran kusoshin JKS da gwamnatin kasar da kuma wakilan jama'ar kasar kusan dubu 3 suka halarta.
A yayin bikin bude taro na 2 na majalisar NPC karo na 13 a yau, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya karanta rahoto game da ayyukan da gwamnatinsa ta yi a shekarar 2018, zai kuma fitar da shiri kan ayyukan da za a yi a bana domin wakilan jama'ar su duba tare da tattaunawa kansu. (Tasallah Yuan)