in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministar Birtaniya ta dage kada kuri'ar ficewar kasar daga EU zuwa ranar 12 ga watan Maris
2019-02-25 13:34:10 cri

Firaministar Birtaniya Theresa May, ta tabbatar da kara dage kada kuri'a kan yarjejeniyar ficewar kasar daga kungiyar Tarayyar Turai zuwa ranar 12 ga watan Maris

Da take ganawa da manema labarai a kan hanyarta ta zuwa Sharm el-Sheikh na Masar, domin halartar taron Tarrayar Turai da na kungiyar kawancen Larabawa, Theresa May ta soke batun gabatar da yarjejeniyar ga 'yan majalisar dokokin kasar a wannan mako.

Firaministar ta bayyana cewa, tawagarta za ta koma Brussels a ranar Talata. A don haka, ba za su samu kuri'ar da suke bukata ba a wannan mako, amma za su tabbatar da hakan a ranar 12 ga watan Maris.

Har ila yau, ta ce har yanzu batun barin EU a ranar 29 ga watan Maris ya na hannunsu, kuma shi ne abun da suke shirin yi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China