in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokoin Birtaniya ta kada kuri'ar kin amincewa da kudurin Firaministar kasar na ficewa daga EU
2019-02-15 10:27:55 cri
Majalisar dokokin Birtaniya, ta kada kuri'ar kin amincewa da kudurin da Firaministar kasar Theresa May ta gabatar, wanda ke kunshe da dabarun gwamnati na ficewar kasar daga Tarayyar Turai.

'Yan majalisar sun kada kuri'ar amincewa 258, da na kin amincewa 303, wanda kuma ke jaddada cewa 'yan Majalisar na sane da tattaunawar dake tsakanin Birtaniya da Tarayyar Turai game da iyakar arewacin Ireland da Jamhuriyar Ireland.

Masu ra'ayin rikau kuwa sun kauracewa kada kuri'ar ne bisa dogaro da cewa, kudurin na nufin soke batun cimma yarjejeniya game da ficewar Birtaniya daga Tarayyar Turai.

Shugaban Jam'iyyar Labor Jeremy Corbyn, ya yi kira ga Firaministar da ta amince dabararta ta ficewar kasar daga EU ta sha kaye.

Ya ce kuri'u sun nuna cewa matakin na Firaministan ba shi da rinjaye. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China