in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministar Birtaniya ta yi kira ga majalisar dokokin kasar da ta nuna goyon baya ga yarjejeniyar janyewa daga EU
2019-01-15 14:24:28 cri
Firaministar kasar Birtaniya Theresa May, ta yi kira ga membobin majalisar wakilan kasar, da su jefa kuri'un goyon baya ga yarjejeniyar janyewa daga kungiyar EU.

A ranar 15 ga wata, majalisar wakilai ta kasar Birtaniya za ta jefa kuri'u game da yarjejeniyar janyewa daga kungiyar EU, wadda gwamnatin kasar Birtaniya da kungiyar EU suka cimma daidaito.

A ranar 14 ga wata, May ta yi kashedi cewa, idan majalisar wakilai ta kasar ta ki amincewa da yarjejeniyar, yadda Birtaniya ta gaza janyewa daga kungiyar EU, hakan zai kawo illa ga imanin al'ummun kasar ga gwamnati.

May ta kara da cewa, wasu membobin majalisar suna son jinkirta, ko dakatar da janyewa daga kungiyar EU. Idan aka dakatar da yarjejeniyar, watakila kasar Birtaniya ba za ta janye daga kungiyar EU ba, yiwuwar batun ya fi yiwuwar janyewa daga kungiyar EU ba tare da cimma yarjejeniyar ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China