in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Birtaniya za ta jefa kuri'a kan yarjejeniyar ficewar kasar daga EU
2019-01-09 10:00:36 cri
Fadar firaministan kasar Birtaniya ta tabbatar jiya Talata cewa, majalisar wakilan kasar za ta jefa kuri'a a ranar 15 ga wata kan yarjejeniyar ficewar kasar daga tarayyar Turai wato EU wanda aka sha jinkirta wa.

Tun a watan Disamban bara ne majalisar wakilan kasar ta kuduri aniyar jefa kuri'a game da yarjejeniyar ficewar kasar daga EU da gwamnatin Birtaniya da EU suka cimma. Amma a jajibirin ranar jefa kuri'ar, firaministar kasar Teresa May ta sanar da dage jefa kuri'ar ba zato ba tsammani, bisa dalilin cewar, akwai yiwuwar ba za'a amince da yarjejeniyar ba.

Teresa May ta jaddada cewa, 'yan majalisar wakilan kasar da dama sun goyi bayan wasu muhimman abubuwa da dama dake kunshe cikin wannan yarjejeniya, amma kuma sun nuna damuwa sosai kan batun iyakokin Birtaniya da Ireland bayan da ta fice daga EU.

Bisa yarjejeniyar da aka cimma a baya, Birtaniya za ta fice daga EU a ranar 29 ga watan Maris din bana.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China