in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban magatakardan MDD ya nada jami'in diflomasiyyar Sin a matsayin manzon musamman mai kula da harkokin yankin manyan tafkunan Afirka
2019-01-23 09:49:14 cri
Mataimakin kakakin babban magatakardan MDD Farhan Haq ya bayyana a jiya Talata cewa, babban magatakardan MDD Antonio Guterres ya sanar da nada jami'in diflomasiyyar kasar Sin Xia Huang a matsayin manzon musamman nasa mai kula da harkokin yankin manyan tafkunan nahiyar Afirka.

Xia Huang ya shafe shekaru 30 yana aikin diflomasiyya, ya kuma yi aiki a kasashen Afirka da dama. Daga shekarar 2015 zuwa shekarar 2018, ya zama jakadan kasar Sin a kasar Congo-Brazzaville.

Yankin manyan tafkuna Afirka dai yana tsakiyar gabashin nahiyar Afirka, wato yankunan dake kewaye da kuma kusa da tabkin Victoria, tabkin Tanganyika da kuma tabkin Kivu.

A halin yanzu, yankin ya kasance wurin dake fama da matsalolin rikice-rikice, karancin abinci, da kuma 'yan gudun hijira, sakamakon hare-haren da suka addabi yankin. Lamarin da ya sa ake kira yankin "gangar albarushi na nahiyar Afrika". (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China