Ministan harkokin waje na kasar Sin zai kai ziyarar aiki wasu kasashen Afirka
A yau Jumm'a mai magana da yawun ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Madam Hua Chunying ta sanar da cewa, bisa goron gayyatar da takwaransa na kasar Habasha, da shugaban hukumar zartaswar kungiyar tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat, da ma takwarorinsa na Burkina Faso da Gambia da kuma Senegal suka yi masa, daga ranar 2 zuwa 6 ga watan Janairu mai zuwa, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin wanda kuma shi ne ministan harkokin waje na kasar, Wang Yi zai kai ziyarar aiki kasashen da ma kungiyar tarayyar Afirka. (Lubabatu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku