in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sanannun 'yan jaridun kasashen dake hanyar siliki sun yabawa Sin kan aikin yaki da ta'addanci
2019-01-12 16:25:35 cri
A ranar 10 ga wata, wasu sanannun 'yan jarudun kasashen dake kan hanyar siliki suka fara ziyara a jihar Xinjiang ta kasar Sin. Ziyarar da babban gidan talabijin da rediyo na kasar Sin wato CMG da ofisoshin jakadancin Sin dake kasashen da abun ya shafa suka shirya tare, tana kunshe da wasu sanannun 'yan jaridu wadanda suka zo daga wasu kasashe 6, ciki har da Masar, da Turkiyya, da Pakistan, da Afghanistan, da Sri Lanka da kuma Bangladesh.

Bayan wadannan 'yan jaridu sun ziyarci dakin nune-nunen harkokin yaki da ta'addanci na jihar Xinjiang, dukkansu sun bayyana cewa, ta'addanci shi ne abokin gabar dukkanin bil Adama, ya kamata kasashen duniya su yi hadin gwiwa domin fuskantar wannan matsala. Kuma kasar Sin ta dauki matakai yadda ya kamata, wadanda za su tabbatar da zaman lafiya a jihar Xinjiang.

Haka kuma, shugaban kungiyar 'yan jaridu ta Izmir ta kasar Turkiya Misket Dikmen ya bayyana cewa, cikin dogon lokacin da suka gabata, kasar Turkiya tana fama da matsalar ta'addanci, shi ya sa, kasarsa ta fahimci damuwar kasar Sin sosai ta fuskar wannan aiki. Ya ce, nune-nunen da suka kalla a wannan rana, sun nuna tashe-tashen hankula da rasuwar mutane da 'yan ta'adda suka kawo mana. A ganinsa, nunawa al'ummomin kasa da kasa game da mugun laifukan da 'yan ta'adda suka aikata ya kasance wani mataki mai karfi, ta yadda kowa zai gani da idonsa, kuma za a fahimci wannan batu yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China