in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sin ta fidda takardar kiyaye da raya al'adun jihar Xinjiang
2018-11-15 11:02:17 cri
Yau Alhamis ne, ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya fidda wata takarda game da yadda ake kiyaye da raya al'adun jihar Xinjiang, inda ya bayyana cewa, jihar Xinjiang jiha ce mai hade da kabilu da al'adu iri-iri tun da dadewa. Kuma al'adun kabilu daban daban na jihar Xinjiang sun inganta bunkasuwar al'adun dukkanin kabilun kasar Sin baki daya, da zurfafa al'adun Sin.

Cikin takardar, an bayyana cewa, tun bayan kafuwar jamhuriyyar jama'ar kasar Sin, ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar tana mai da hankali kwarai wajen kiyaye da kuma raya al'adun kabilu daban daban dake jihar Xinjiang, ta kuma yi kokarin ganin al'ummomin kabilu daban daban na jihar sun koyi harsunan juna, domin karfafa mu'amalar dake tsakanin al'ummominsu da mutunta 'yancin su na bin ko wane irin addini da kuma inganta harkokin al'adu a jihar, ta yadda al'ummomin kasar za su kara amincewa da kaunar al'adun juna. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China