in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi allah wadai da yadda kafofin watsa labaran ketare ke sukar matakan kasar na yaki da ayyukan ta'addanci a Xinjiang
2018-08-14 19:35:07 cri
Kasar Sin ta zargi wasu kafofin watsa labarai na ketare da watsa rahotanni na son kai game da matakan yaki da ayyukan ta'addanci da kasar ke dauka a yankin Xinjiang na Uygur mai cin gashin kansa.,

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, ya ce wasu kafofi dake adawa da kasar Sin suna kokarin shafa mata kashin kaji ne don biyan bukatunsu na siyasa.

A ranar 10 da kuma 13 ga watan Agusta ne yayin zamansa na 96 kwamitin yaki da nuna wariyar launin fata na MDD ya yi bitar yanayin da ake ciki a kasar ta Sin .

Lu ya ce tawagar kasar Sin yayin zaman ta yi bayani dalla-dalla game da ci gaban da kasar Sin ta samu wajen kare 'yancin kananan kabilu kuma kwamitin ya tabbatar da kokari da ma nasarorin da gwamnatin kasar Sin ta cimma a wannan fanni.

A halin yanzu, komai ya dai-daita a yankin na Xinjiang, yanayin ci gaban tattalin arzikin yankin abin a yaba ne, kana dukkan kabilu na zama da juna cikin lumana. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China