in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta mai da Afirka muhimmin matsayi cikin harkokin diflomsiyya, in ji Wang Yi
2019-01-04 10:55:20 cri
A jiya Alhamis ne mamban majalisar gudanarwa ta kasar Sin, kana ministan harkokin waje Wang Yi, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Habasha Workneh Gebeyehu a birnin Addis Ababa, fadar mulkin kasa ta Habasha. Bayan ganawar tasu, sun gana da 'yan jaridu cikin hadin gwiwa.

Wang Yi ya ce, ministan harkokin wajen kasar Sin ya kan fara ziyarar aiki a ko wace shekara a kasashen Afirka cikin shekaru 29 da suka gabata. Wannan ya kasance kyakkyawar al'adar gargajiya ta fuskar harkokin diflomasiyyar kasar Sin. Ya kuma nuna cewa, kasar Sin ta ci gaba da mai da kasashen Afirka wani muhimmin matsayi cikin harkokin diflomasiyyar ta. Kaza lika karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kasashen Afirka da ma kasashe masu tasowa, shi ne babban burin kasar Sin kan aikin diflomasiyya.

Wang Yi ya ce, an cimma nasarar gudanar da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka a watan Satumba na shekarar 2018. Kuma a wannan karo, ya kai ziyarar aiki a kasashen Afirka, domin aiwatar da sakamakon da aka cimma a yayin taron, ta yadda za a ci gaba da inganta dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka, yayin da ake kyautata dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka bisa manyan tsare-tsare. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China