in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na kasar Sin zai ziyarci wasu kasashen Afirka hudu
2018-12-28 19:20:33 cri
Mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, zai ziyarci wasu kasashen Afirka hudu bisa gayyatar da da shugaban hukumar zartaswar kungiyar tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat, da takwarorin sa na kasar Habasha Workneh Gebeyehu, da na Burkina Faso Alpha Barry, da na Gambia Mamadou Tangara, da kuma na Senegal Sidiki Kaba suka yi masa.

Wang Yi zai fara da ziyarar aiki ne a kasar Habasha, inda kuma zai ziyarci hedkwatar kungiyar AU dake birnin Addis Ababa, sa'an nan ya isa kasashen Burkina Faso, da Gambia da Senegal tsakanin ranekun 2 zuwa 6 ga watan Janairu dake tafe.

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Madam Hua Chunying ta sanar da hakan a yau Juma'a, yayin taron manema labarai da ya gudana a birnin Biejing.

Ta ce ministan yana zabar kasashen Afirka a matsayin yankin da zai fara kaiwa ziyara a duk shekara, kuma ziyarar ta wannan karo, ci gaba ne ga wannan kyakkyawar al'ada, wadda ke shaida irin muhimmanci da Sin ke baiwa hadin gwiwar ta da kasashen nahiyar Afirka.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China