Haka kuma, an ce, ya zuwa karfe 2 da rabi na yammacin jiya Laraba, masu ayyukan ceto sun riga sun gano mutane 27 a karkashin burabuzan gini, ciki har da mutane 21 da suka rasu, da kuma mutane 6 da suka ceto. Kuma cikin wadanda suka rasa rayukansu akwai jarirai guda biyu.
Ban da haka kuma, masu aikin ceton suna ci gaba da neman sauran mutane 20 da suka bace.
Bisa labarin da aka samu, an ce, an gina wannan ginin bene mai hawa 10 ne a shekarar 1973, wani sashe na ginin ya rushe gaba daya sakamakon fashewar iskar gas. (Maryam)