in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta ce Amurka na sane da yadda take martaba yarjejeniyar hana kera makamai masu cin matsakaicin zango
2018-12-05 10:45:55 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha, ta ce Amurka na sane da yadda Rashan ke biyayya ga yarjejeniyar hana kera makaman kare-dangi masu cin matsakaicin zango ta INF. Wadannan kalamai dai na zuwa ne bayan da Amurka da kawayanta, suka yi kira ga Rashan da ta kara azama, wajen aiwatar da wannan yarjejeniya yadda ya kamata.

Mai magana da yawun ma'aikatar Maria Zakharva ce ta yi wannan tsokaci, bayan da sakataren wajen Amurka Mike Pompeo ya gabatar da wancan kira ga Rasha, yayin wani taron manema labarai da ya gudana a birnin Brussels. Mr. Pompeo dai ya ce kasar sa za ta jingine biyayyarta ga yarjejeniyar INF nan da kwanaki 60, muddin dai Rasha ba ta koma aiki da yarjejeniyar yadda ya kamata ba.

A watan Oktoba ma dai shugaban Amurka Donald Trump, ya yi barazanar janyewa daga wannan yarjejeniya, bisa zargin cewa Rasha na kauracewa aiki da ita. To sai dai kuma Rashan ta sha musanta wannan zargi. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China