in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin tekun Morocco sun ceto 'yan gudun hijira guda 367 a tekun bahar Rum
2018-12-28 10:59:57 cri
Rundunar sojan kasar Morocco ta sanar a jiya Alhamis cewa, sojojin tsaron tekun kasar sun taimakawa jiragen ruwa da dama a tekun bahar Rum, wadanda suke dauke da wasu mutane 367,wadanda ke da niyyar kutsa kai cikin harabar nahiyar Turai ta wata barauniyar hanya, ciki har da mata da yara.

Bayanai na cewa, galibin bakin hauren da aka ceto sun fito ne daga kasashen Afirka dake kudu da Hamadar Sahara, kuma an riga an kai su tashoshin jiragen ruwa dake kusa.

Ko da a kwanan baya ma, sojojin tsaron tekun kasar Morocco sun karfafa aikin sintiri a yankin tekun dake arewacin kasar, sakamakon karuwar matsalolin masu satar shigowa a yankin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China