Rahotanni daga kasar Morocco na cewa, 'yan ci ranin na cikin wasu kwale kwalen roba ne guda hudu, sun kuma kunshi mata da yara kanana.
Tun daga farkon wannan shekara ta 2018, kasar Morocco ke fuskantar karuwar masu yunkurin tsallakawa Turai ta sassan tekun ta. (Saminu)