in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AfDB, da asusun kasar Sin sun baiwa Morocco rancen dala miliyan 138.6 don samar da ruwan sha
2018-12-22 15:44:07 cri
Bankin raya cigaban Afrika (AfDB) da asusun kasar Sin na raya cigaban Afrika (AGTF) sun samar da rancen kudade ga kasar Morocco sama da euro miliyan 122 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 138.6 domin taimakawa kasar Morocco don inganta aikin samar da ruwan sha.

A ranar juma'ar data gabata ne aka sanya hannu kan yarjejeniyar bada rancen a Rabat babban birnin kasar, wanda babban daraktan hukumar samar da lantarki da ruwan sha na kasar, Abderrahim El Hafidi, da wakiliyar bankin AfDB a Morocco, Leila Mokadem suka jagoranci sanya hannu kan yarjejeniyar.

Yarjejeniyar ta kunshi samar da rance kudi euro miliyan 79.33 wanda bankin AfDB ya samar, sai kuma kashi na biyu na euro miliyan 43.36 wanda asusun kasar Sin na AGTF ya samar.

AGTF wani asusu ne dake samar da kudi dala biliyan 2 wanda ke tallafawa ayyukan da AfDB da bankin People's Bank of China suke gudanarwa wajen raya cigaban kasashen Afrika.

Wadannan basukan kudade za su tallafawa shirin kasar Morocco na samar da ruwa, wanda ya kunshi janyo ruwa daga madatsun ruwan kasar daban daban don tacewa. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China