in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Boko Haram ta yi garkuwa da 'yan mata a kalla 15 na kudu maso gabashin Nijer
2018-11-25 15:20:29 cri
Dan majalisar dokokin kasar Nijer mai wakiltar lardin Diffa dake kudu maso gabashin kasar, Lamido Moumouni ya ce kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da 'yan matan lardin a kalla 15 a daren ranar 23 ga wata, kuma har zuwa yanzu, ba a san inda suke ba.

Lamido Moumouni ya bayyana haka ne jiya a birnin Yamai, fadar mulkin kasar, inda ya ce an sace 'yan matan ne a yankin Toumour na lardin Diffa.

Ya kara da cewa, gwamnatin kasar za ta dauki matakan gaggawa na neman 'yan matan, kuma mai yiyuwa za ta dauki matakan soja a wannan yanki.

Lardin Diffa yana kan iyakar Nijer da Nijeriya, kuma a 'yan shekarun baya-bayan nan, kungiyar Boko Haram ta kai hare-haren ta'addanci da dama a wannan lardi, wadanda suka haddasa mutuwar mutane da dama.

A daren ranar 21 ga wata, kungiyar Boko Haram ta kai hari kan wani kamfanin Faransa dake yankin Toumour dake lardin, harin da ya haddasa mutuwar a kalla guda 6, yayin da mutane 7 suka jikkata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China