in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana zargin Boko Haram da kashe manoma 12 a arewa maso gabashin Najeriya
2018-10-21 16:31:17 cri
An tsinci gawarwakin mutane 12 a wani kauye a jahar Borno, dake arewa maso gabashin Najeriya, bayan wani hari da ake zargin mayakan Boko Haram da kaddamarwa da safiyar ranar Asabar, kamar yadda shugaban kungiyar 'yan sintiri na yankin ya tabbatar.

Gawarwakin 12 da aka tsinto suna da munanan raunuka a jikinsu, inji Kolo Babakura, shugaban jami'an tsaron sa kai na fararen hula.

Kolo yace, an kashe mutanen ne a lokacin da suke tsaka da gudanar da ayyuka a gonakinsu dake kauyen Kalle wadanda mayakan suka isa wajen a cikin manyan motoci biyu inda suka afkawa manoman, inda daga bisani maharan suka tsere cikin daji dake kusa da kauyen.

Babakura yace, akwai yiwuwar za'a iya samun karin wasu gawarwakin, kasancewar ana cigaba da bincike a kauyen.

Rundunar sojojin Najeriya ma ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa data fitar a jiya Asabar. Sai dai, rundunar sojojin tace gawarwakin mutane biyu kawai aka samu ya zuwa yanzu.

Ta kara da cewa, babu wani rahoton yin garkuwa da mutane da aka samu bayan kaddamar da harin.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China