in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunonin sojin Kamaru da Nijeriya sun amince su hada hannu wajen yaki da Boko Haram
2018-10-27 15:22:33 cri
Rundunonin sojin Kamaru da Nijeriya, sun amince su ci gaba da aiki tare wajen yakar kungiyar Boko Haram, kungiyar 'yan ta'adda dake da mazauni a yankin arewa maso gabashin Nijeriya, wadda kuma ke gudanar da muggan ayyukanta a yankin arewa mai nisa na Kamaru da kuma kasashen Chadi da Nijer.

Wata sanarwa da rundunar sojin Nijeriya ta fitar a jiya, ta ce rundunonin sojin biyu za su yi aiki tare wajen murkushe ragowar 'yan kungiyar Boko Haram dake iyakokinsu, musammam ta hanyar kaddamar da ayyukan soji na hadin gwiwa.

Sanarwar ta kara da cewa, dakarun kasashen biyu za su zage damtse ba tare da yin kasa a gwiwa ba, ga ayyukansu na kan iyakoki, wajen ganin sun dakile duk wasu ayyukan mayakan Boko Haram.

A baya, rundunonin biyu sun gudanar da ayyukan hadin gwiwa kan kungiyar Boko Haram a dajin Sambisa da yankin tafkin Chadi, inda kungiyar ke da manyan sansanonin horo. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China