Sanarwar da rundunar sojin kasar ta fitar a shafinta na Twitter, ta ce dakarun na briget ta 21 na aikin sintiri ne a lokacin da mayakan suka yi musu kwantar bauna, a kan titin Maiduguri zuwa Bama na jihar, inda ta ce an yi musayar wuta sosai tsakanin bangarorin biyu.
Hotunan da rundunar ta wallafa sun nuna an kashe akalla mayakan boko Haram 3, tare da kwato makamai da alburusai.
Sanarwar ta kara da cewa, har yanzu dakarun na aikin sintiri a yankin da nufin nemo mayakan da suka tsere da raunuka.
Ko a daren Larabar da ta gabata, an kashe mayakan Boko Haram da dama a garin Damasak dake jihar ta Borno, biyo bayan ba-ta-kashin da suka yi da sojoji. (Fa'iza Mustapha)