in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jaridun Philippines sun gabatar da sharhi na Xi Jinping
2018-11-19 16:16:54 cri
Yau Litinin, kafin ziyararsa a kasar Philippines, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya rubuta wani sharhi mai taken "Yin hadin gwiwa domin raya sabuwar dangantaka a tsakanin Sin da Philippines" a wasu jaridun kasar da suka hada da jaridar Philippine Star, jaridar Manila Bulletin da kuma jaridar Daily Tribune.

Cikin sharhin, shugaba Xi ya bayyana cewa, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka kan ka'idar yin hadin gwiwa domin cimma moriyar juna, da kuma kara bude kofa ga waje. Kuma Sin tana maraba ga kasar Philippines da sauran kasashen duniya da su yi hadin gwiwa da ita wajen neman ci gaba cikin sauri. A nan gaba kuma, kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa da sassa daban daban, domin kiyaye tsarin cinikin dake tsakanin kasa da kasa bisa jagorancin kungiyar WTO, da kuma raya tsarin siyasa da tattalin arzikin duniya cikin yanayin adalci. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China