in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya kai ziyarar aiki kasar Brunei
2018-11-19 10:29:46 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya isa Brunei a jiya Lahadi domin ziyarar aiki. karon farko cikin shekaru 13 da shugaban kasar Sin ya kai ziyara kasar dake kudu maso gabashin Asiya.

A madadin gwamnatin kasar Sin da al'ummarta, Xi Jinping ya mika gaisuwa da fatan alkhairi ga gwamnatin Brunei da al'ummarta.

Shugaba Xi ya kuma jadadda cewa, kasar Sin da Brunei makotan juna ne kuma aminai, kana abokan hulda da suka aminta da juna, la'akari da daddadiyar huldar abota dake tsakaninsu.

Kasar ita ce waje na biyu da Shugaban Sin ya ziyarta a rangadin da yake a yankin Asiya da Fasifik. Da farko, ya kai ziyarar aiki kasar Papua New Guinea, inda ya gana da shugabanni daga kasashen tsibirin Fasifik dake da huldar jakadanci da kasar Sin, tare da halartar taron shugabannin Asiya da Fasifik kan harkokin tattalin arziki da masana'antu a Port Morseby, babban birnin kasar Papua New Guinea. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China