Wannan ce dai ziyarar farko da wani shugaban kasar Sin ya kai kasar, tun bayan da kasashen biyu suka kulla huldar diflomasiyya tsakanin su a shekarar 1976.
Yayin ziyarar da ya fara, shugaban zai kuma gana da shugabannin kasashen yankin 8, da suka kulla hulda da Sin a birnin Port Moresby, fadar mulkin Papua New Guinea.
Papua New Guinea ce zangon farko, a ziyarar da shugaban na Sin zai yi a wannan yanki, inda daga bisani zai ziyarci Brunei da kuma kasar Philippines.