in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Morocco za ta fitar da baki 141 na kasashen Afirka dake kudancin Sahara daga kasarta
2018-10-23 11:01:48 cri
Gwamnatin kasar Morocco, ta fidda sanarwar cewa, za ta fitar da bakin kasashen Afirka dake kudancin hamadar Sahara guda 141 daga kasarta.

Bisa labarin da aka samu, an ce, 'yan sandan kasar Morocco sun kama wadannan baki ne a lokacin da suke kokarin keta shingen da aka dasa a yankin iyakar dake tsakanin kasar Morocco da birnin Melilla na kasar Spaniya a ranar 21 ga wata. Kana, a wannan rana, mutane sama da dari 3 sun shirya keta yankin iyakar dake tsakanin birnin Melilla da kasar Morocco, wasu daga cikinsu sun cimma nasarar shiga birnin, yayin da 'yan sandan kasar Morocco suka kama mutane 141 daga cikinsu.

Bugu da kari, an ce, wani bako ya rasu sakamakon faduwar da ya yi daga kan shingen, yayin da baki 22 suka jikkata a lokacin da suka keta shingen, inda aka kai su asibiti. Ban da haka kuma, sojojin kasar Morocco sama da goma sun ji rauni a yayin da suka dukufa wajen hana wadannan baki keta shingen. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China