in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco da Benin sun sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa game tsara samar da gidaje da raya birane
2018-10-06 15:23:11 cri
Mahukuntan kasashen Morocco da Benin, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa ta shekaru 3, wadda ta shafi yin musayar dabarun samar da gidaje da raya birane.

Ministan ma'aikatar bunkasa birane, samar da gidaje da tsara ci gaban birane na kasar Morocco Abdelahad Fassi Fihri, da ministan kyautata muhalli da samar da ci gaba mai dorewa na kasar Benin Jose Tonato ne suka sanya hannu kan takardun yarjejeniyar.

Da yake tsokaci game da hakan, yayin bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar a birnin Rabat, fadar mulkin kasar Morocco, Mr. Fassi Fihri, ya jaddada muhimmancin wannan yarjejeniya, yana mai cewa za ta baiwa kasashen biyu damar amfana da kwarewar juna, a fannin warware matsalolin bunkasa ci gaban birane.

A nasa bangare kuwa, Mr. Tonato cewa ya yi, kasar sa na fatan amfana daga kwarewar Morocco a fannin tsara manufofin kyautata yankunan ta. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China