in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco za ta kaddamar da jirgin kasa mai sauri na farko a Afrika zuwa karshen shekarar nan
2018-07-13 09:54:13 cri
Hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Morocco, ta ce kafin karshen shekarar nan, kasar za ta kaddamar da jirgin kasa mafi sauri na farko a Afrika.

Sanawar da hukumar ta fitar, ta ce an fara shirye-shiryen kaddamar da layin dogon mai sauri da ya hada birnin Tangier, dake gabar teku da Casablanca, cibiyar harkokin kasuwanci ta kasar tun a watan Yuni.

Hukumar ta ce a ranar Litini za a kaddamar da gasar tsara tambarin jirgin ga duk wanda ke son bada gudunmuwa ga aikin da kasar ta yi domin al'ummarta.

Sabon jirgin dake gudun da ya zarce kilomita 352 cikin kowacce sa'a, zai rage tsawo lokacin da ake dauka yayin tafiya tsakanin Tangier da Casablanca daga sa'o'i 5 zuwa kimanin 2.

An shafe shekaru 10 ana aikin da ya lakume dala biliyan 2, wanda aka samu daga Moroocon da Faransa da Saudiyya da Kuwait da Hadaddiyar Daular Laraba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China