in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyoyin masana'antu da kasuwanci na Sin sun sanar da kin takardar B20
2018-10-06 16:19:34 cri
Jiya Jumma'a, an kammala taron kolin harkokin masana'antu da kasuwanci na kungiyar G20, watau B20 na shekarar 2018 a birnin Buenos Aires na kasar Argentina. Bayan taron, kungiyoyin masana'antu da kasuwanci na kasar Sin sun fidda wata sanarwa, inda suka nuna kiyayarsu kan takardar ba da shawara kan manufofi da B20 ta gabatarwa.

Kwamitin raya ciniki tsakanin kasa da kasa na kasar Sin, da kwamitin harkokin masana'antu da kasuwanci na kasar Sin dake B20, sun fidda wata sanarwa a madadin kungiyoyin masana'antu da na kasuwanci, suna masu cewa, sun halarci wannan taro cikin himma da kwazo, inda suka ba da shawarwari masu amfani da dama, kan batutuwan da aka tattauna a yayin taron. Sun kuma bayyana ra'ayoyin kasar Sin kan kyamar kariyar ciniki, da inganta kwaskwarima ga kungiyar WTO yadda ya kamata, da dai sauransu. Haka kuma, sau da dama, sun tattauna da mashirya taron, inda suka gabatar da shawarwarinsu kan yadda za a gyara takardar.

Amma cikin sanarwar da suka fitar, an ce, taron B20 ta musanta bukatun da kungiyoyin masana'antu, da na kasuwanci na kasar Sin suka gabatar mata, cikin takardar da B20 ya fitar, bai nuna ra'ayoyinsu yadda ya kamata ba, lamarin da ya lahanta ka'idar yin shawarwari domin cimma matsaya guda ta taron B20. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China