An gudanar da taron koli na 12 na shugabannin kungiyar G20 ta kasashe masu karfin tattalin arziki a birnin Hamburg na kasar Jamus a jiya Jumma'a, inda shugaban kasar Sin Mista Xi Jinping ya halarci taron tare da yin jawabi mai taken "Nacewa ga bude kofa da hakuri da juna don sa kaimi ga hadin gwiwa da ci gaba".
A cikin jawabinsa, shugaban na kasar Sin ya jaddada cewa, ya kamata kungiyar G20 ta tsaya kan kokarin tabbatar da yanayin tattalin arzikin duniya irin na bude kofa, da neman sabbin hanyoyin da za su taimakawa raya tattalin arziki, da amfani da habakar tattalin arziki ta yadda karin bangarori za su mora, da daidaita tsarin kula da harkokin tattalin arzikin duniya, don neman samun walwala ta bai daya, da kulla wani kawance bisa tushen makomar bai daya ta bil Adama.