in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya gana da firaministan Japan kan kyautata huldar dake tsakaninsu
2017-07-08 17:35:58 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana a yau Asabar, da firaministan Japan Shinzo Abe kan dangantakar dake tsakanin kasashensu, a wani bangare na taron kungiyar G2O dake gudana a birnin Hamburg na Jamus.

Xi Jinping ya bukaci Japan ta dauki darasi daga tarihi domin samun makoma mai kyau, inda ya ce ya kamata Shinzo Abe ya kawar da duk wani tarnaki domin kyautata huldar dake tsakaninsu.

Shugaban na Sin ya kuma nemi Japan ta dauki ingantattun matakan da za su tabbatar da zaman lafiya da kawance tsakanin kasashen biyu.

Har ila yau, shugaba Xi wanda ya ce kasarsa na maraba da Japan ta shiga shawarar 'ziri daya da hanya daya', ya ce babu batun yarjejeniya game da abun da ya wuce da kuma yankin Taiwan, yana mai bukatar Japan ta daraja furucin da ta yi.

A nasa bangaren, Firaministan Japan Shinzo Abe ya ce a shirye yake ya yi hasashen makoma mai kyau tare da inganta huldarsa da kasar Sin, inda ya yi alkawarin ba zai sauya matsaya game da yankin Taiwan na kasar Sin ba.

Bugu da kari, ya yi fatan cewa za a inganta musayar ra'ayi da harkokin cinikayya da hada-hadar kudi da yawon bude ido tsakanin Japan da kasar Sin (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China