in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyya mai son raba yankin Taiwan daga kasar Sin ita ce ke bata halin da Taiwan ke ciki, in ji ministan harkokin wajen Sin
2018-09-22 16:43:14 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwaransa na kasar Dominican Miguel Vargas, sun gana da 'yan jaridu cikin hadin gwiwa, inda Wang Yi ya amsa tambayar da 'yan jaridun suka yi masa game da batun lardin Taiwan na kasar Sin.

'Yan jaridun sun nemi jin ra'ayin Wang Yi, game da tsokacin da wasu kasashe da bangarori suka yi a kwanakin baya, na cewa kulla huldar diflomasiyya da kasar Sin da wasu kasashe suka yi, ciki har da kasar Dominican, ya sauya halin da lardin Taiwan ke ciki, kuma zai haddasa illa ga kiyaye yanayin zaman lafiya da ci gaban lardin.

Da yake amsa tambayar, Mr. Wang ya bayyana cewa, kasar Sin kasa ce daya tilo a duniya, kuma lardin Taiwan, daya ne daga cikin yankunan kasar, don haka, ba za a iya raba su ba. Ya ce gamayyar kasa da kasa sun riga sun cimma matsaya guda kan wannan batu. Kuma kulla dangantakar diflomasiyya da Kasar Dominican da wasu kasashen duniya suka yi da kasar Sin, ya dace halin da ake ciki yanzu, kuma abu ne mai kyau da ya dace da moriyar al'ummomi da kasar Dominican.

Dangane da batun "sauya halin da lardin Taiwan yake ciki" kuwa, ya ce ya kamata a halin yanzu, jam'iyyar Min Jin, mai mulkin lardin Taiwa, ta ba ta tsayar da yunkurin raba lardin daga kasar Sin ba, kuma ayyukan da ta ke yi, sun bata huldar dake tsakanin lardin Taiwan da babban yankin kasar Sin, da kuma halin da lardin Taiwan yake ciki, wato na kasancewarsa lardin kasar Sin, ba wata kasa ta daban ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China