in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron kolin FOCAC na Beijing ta karfafa hadin kan Sin da kasashen Afirka da tabbatar da ci gabansu tare
2018-09-06 20:56:09 cri
Yau Alhamis, ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya zantawa da manema labaru, inda ya yi bayani a kan taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka wato FOCAC da aka shirya a nan birnin Beijing, da kuma nasarorin da aka cimma a gun taron.

Wang ya ce, taron kolin ya kasance taron diplomasiyya ne mafi kasaita Sin ta taba karbar bakuncinsa. A karkashin jagorancin shugaban kasar Sin Xi Jinping, Sin da kasashen Afirka sun yi hadin kai da sahihiyar zuciya, har ma sun cimma jerin nasarori masu ma'ana. Kaza lika taron kolin ya kasance alama ta karfafa hadin kai, da neman ci gaba tare a tsakanin Sin da kasashen Afirka. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China