in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya gana da zababbiyar shugabar zauren MDD, inda ya yi kira da a daukaka huldar kasa da kasa
2018-08-07 09:45:35 cri
Mamba a majalisar gudanarwar kasar Sin, kuma Ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gana a jiya Litinin, da zababbiyar shugabar zaure na 73 na MDD, Maria Fernanda Espinosa Garces, inda ya yi kira da a karfafa cimma ra'ayi daya kan huldar kasa da kasa da kuma kiyaye iko da ayyukan MDD.

Wang Yi, ya ce ya kamata al'ummomin duniya su kiyaye tsarin huldar kasa da kasa bisa manufofi da ka'idojin da MDD ta gindaya, tare da kokarin bunkasa tattalin arzikin duniya ta kowacce fuska kuma a bayyane, sannan bisa daidaito da adalci ta yadda kowa zai mora.

Ya kuma yi kira da a yi adawa da ra'ayi na kashin kai da kariyar cinikayya, tare da kare dokokin kasa da kasa da muradun jama'ar duniya.

A nata bangaren, Espinosa Garces, ta yabawa muhimmiyar rawar da Sin ke takawa wajen goyon bayan huldar kasa da kasa da ayyukan MDD.

Ta kuma yabawa shawarar 'Ziri Daya da Hanya Daya' inda ta bayyana ta a matsayin kyakkyawar gudunmuwar da za ta bunkasa ci gaban duniya, ta na mai cewa, za ta ci gaba da marawa shawarar baya, kana ta na sa ran kara karfafa hadin gwiwa da kasar Sin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China