Kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ba da muhimmin umurnin cewa, ya kamata a mai da hankali kan kiyaye idanun yaran kasar Sin, sabo da cikin shekarun baya bayan nan, ana samun karin daliban da suke fama da matsalar kasa ganin abubuwa masu nisa, kuma shekarun daliban da suke fara gamuwa da wannan matsalar yana raguwa, lamarin da ya haddasa rashin lafiyar jikunam da zukatan yaran kasar.
Don haka Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata dukkanmu mu dauki matakai yadda ya kamata, domin kiyaye idanun yara cikin hadin gwiwa, ta yadda za su sami wata makoma mai haske. (Maryam)