in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Kurdawa sun amince da yin shawarwari da gwamnatin Syria
2018-07-30 10:52:19 cri
Kwamitin dimokuradiyya na Syria, watau wata hukumar siyasa da dakarun Kurdawa suka kafa, ya fidda wata sanarwa a ranar 28 ga wata cewa, kwamitin ya yarda da kafa kwamitin yin shawarwari tare da gwamnatin kasar Syria, domin share fagen yin shawarwarin da za a yi tsakanin bangarorin biyu gaba.

A halin yanzu, rundunar sojojin dimokuradiyya mai adawa da gwamnati dake karkashin jagorancin dakarun Kurdawan, ta mamaye galibin yankunan dake arewa da kuma gabashin kasar.

Bisa labarin da aka samu, an ce, tawagar wakilan kwamitin dimokuradiyyar Syria ta yi shawarwari da wakilan gwamnatin kasar a ranar 26 ga wata, inda a fili ne suka tattauna batun yankunan da dakarun Kurdawan suka mamaye a arewa da kuma gabashin kasar karo na farko.

Sa'an nan, kwamitin dimokuradiyyar ya sanar a ranar 28 ga wata cewa, shi da gwamnatin kasar sun cimma matsaya guda, kan kafa wata kasa mai bin salon dimokuradiyya, da aka rarraba ikonta tsakanin sassa.

Bugu da kari, an fidda rahoto cewa, sojojin gwamnatin kasar Syria sun sami ci gaba kan aikin yaki da kungiyar IS a yankin Yarmuk dake kudancin kasar. Kuma, an ce, bi da bi sojojin gwamnati sun kwato garuruwa guda 8 dake yankin Yarmuk, bayan suka kai hari a yankin dake karkashin ikon kungiyar IS dake yammacin lardin Daraa na kasar. Sai dai kuma ya zuwa yanzu, akwai sauran garuruwa da kauyuka guda 6 dake kudu maso yammacin kasar Syria wadanda ba a kwato su ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China