in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata mu girmama 'yancin kan Syria, in ji wakilin Sin
2018-07-27 13:43:38 cri
Manzon musamman kasar Sin mai kula da harkokin Syria Xie Xiaoyan, wanda a halin yanzu, yake ziyarar aiki a kasar Syria, ya bayyana a jiya Alhamis cewa, ya kamata a girmama 'yancin kai, da cikakken zaman yankin kasar Syria, kuma kasar Sin tana fatan halartar aikin sake gina kasa Syria yadda ya kamata.

Xie Xiaoyan ya ce, a yayin ziyarar tasa a kasar Syria ta wannan karo, kasashen Sin da Syria, sun cimma matsayi daya kan harkokin inganta yunkurin siyasa, da yaki da ta'addanci, da kula da 'yan gudun hijira, da kuma halartar aikin sake gina kasar ta Syria.

Ya ce kasar Syria ita ma tana fatan Sin za ta ba da taimako, kan ayyukan warware matsalar kasar ta hanyar siyasa, musamman ma kan harkokin kula da 'yan gudun hijira, da kuma sake gina kasar da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China