Wata sanarwa da rudunar sojan kasar Syria ta fitar, ta ce dakarun kasar da kawayenta sun kai wasu hare-hare kan wasu yankuna dake hannun mayakan IS a lardin Deir al-Zour dake gabashin kasar, inda suka yi nasarar kwato yankunan dake wajen Deir al Zour yamma da birnin al Bukamal a kusa da kan iyakar kasar Iraki.
Wannan dai wani bangare ne na matakan sojan da sojojin Syriar ke dauka a yankin hamadar gabashin kasar, inda a 'yan kwanakin nan sojojin suka yi nasarar sake kwace yankuna masu tarin yawa.(Ibrahim)