in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yang Jiechi ya halarci taron wakilan harkokin tsaron kasashen BRICS karo na 8
2018-06-30 16:37:26 cri
Wakilin ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na JKS Yang Jiechi, ya halarci taron wakilan harkokin tsaron kasashen BRICS karo na 8 da aka yi a birnin Durban na kasar Afirka ta Kudu. An gudanar da taro ne domin share fagen taron shugabannin kasashen BRICS da za a yi a birnin Johannesburg a watan Yuli mai kamawa, da kuma musayar ra'ayoyi kan manyan batutuwan da suka shafi yanayin kasa da kasa da na shiyya-shiyya, da karfafa hadin gwiwar kasashen BRICS a fannonin kiyaye zaman lafiya da yaki da 'yan ta'adda da tsaron yanar gizo da dai sauransu.

A yayin taron, Yang Jiechi ya bayyana cewa, ya kamata kasashen BRICS su karfafa hadin gwiwarsu a fannonin kiyaye zaman lafiya da inganta ci gaba da kuma harkokin kasa da kasa yadda ya kamata, domin ba da gudummawa ta fuskar tsaro da zaman karko a duniya.

Ya kuma jaddada cewa, ganawar da shugabannin kasashen BRICS suka yi a birnin Xiamen na kasar Sin a bara, ta bude wani sabon shafin hadin gwiwar kasashen cikin shekaru 10 masu zuwa. Ya ce ya kamata a aiwatar da ra'ayi daya da shugabannin kasashen suka cimma da kare ka'idojin MDD da tsayawa tsayin daka wajen warware sabanin dake tsakanin kasa da kasa a siyasance da karfafa hadin gwiwa a fannin kare tsarin siyasa da moriyar kasashe masu tasowa da kasashe masu samun saurin ci gaban tattalin arziki, ta yadda za a gina sabuwar dangantaka tsakanin kasa da kasa da kuma karfafa dunkulewar duniya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China