in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron BRICS zai bada damar cudanya tsakanin kasashe
2018-06-29 09:34:20 cri
Firimiyan lardin Guateng na Afrika ta Kudu wato David Makhura, ya bayyana taron kungiyar BRICS da zai gudana a kasarsa, a matsayin wanda zai bada dama ga kasar da nahiyar Afrika ta koyon ingantattun sana'o'i da kirkire kirkire daga kasashen kungiyar BRICS.

David Makhura, ya bayyana haka ne yayin rufe taron kungiyar matasa ta diflomasiyya na kasashen BRICS a Johannesburg.

Ya ce Afrika ta kudu na farin cikin karbar bakuncin taron domin a cewarsa, zai ba 'yan kasuwa damar cudanya da takwarorinsu na kasashen BRICS, ya na mai cewa za su tabbatar da an gudanar da wasu taruka na daban, inda 'yan kasuwa za su samu abun koyo daga takwarorinsu na kasashen BRICS.

Ya kara da cewa, ya kamata nahiyar Afrika ta yi amfani da damar kasancewar Afrika ta kudu cikin kungiyar domin moriyarta, ya na mai cewa kasashen BRICS su ne jigo a fannin ci gaban fasahohi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China