in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shirya taron tattaunawar majalisun dokokin BRICS na bana
2017-10-15 14:09:44 cri
Jiya ranar 14 ga wata, an shirya taron tattaunawar majalisun dokoki na kasashen BRICS na shekarar 2017 a birnin St. Petersburg. Wannan wani muhimmin aiki ne da kasar Sin ta karbi bakunci a matsayin ta na kasar dake shugabancin BRICS a bana, wanda mai taken 'Kara cudanya da hadin kai tsakanin majalisun dokoki, da tabbatar da nasarorin da aka cimma tsakanin shugabannin kasashen BRICS a yayin tattaunawar Xiamen'.

Mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Wang Ping ne, ya shugabanci taron tattaunawar, shugaban majalisar harkokin lardunan kasar Afirka ta kudu Thandi Modise, da shugaban majalisar dattawan kasar Brazil Eunício Oliveira, da shugaban majalisar Duma ta kasar Rasha Vyacheslav Volodin, da mataimakin shugaba na farko na kwamitin tarayyar kasar Nikolay Fyodorov, da kuma shugaban majalisar dokokin kasar India Sumitra Mahajan sun halarci taron tattaunawar.

A yayin jawabinsa, Zhang Ping ya nuna cewa, kamata ya yi majalisun dokokin kasashen biyar su bi ra'ayin bai daya da aka cimma a yayin taron tattaunawar da aka shirya a birnin Xiamen na kasar Sin, don inganta yin kwaskwarima kan tsarin gudanar da harkokin kasa da kasa, kana da kara yin cudanya kan fasahohin da suka samu wajen gudanar da harkokin kasa, ta yadda za a samar da wani muhallin doka da oda wajen hadin kan kasashen BRICS. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China