in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
BRICS tana samun cigaba, inji gwamnatin Afrika ta kudu
2018-06-28 10:34:50 cri
Gwamnatin kasar Afrika ta kudu ta sanar a jiya Laraba a birnin Pretoria cewa, kungiyar kasashen BRICS tana samun cigaba fiye da yadda ake tsammani wanda ya kunshi makomar da masu hasashe suka yi game da cigaban kungiyar.

Mataimakiyar ministar harkokin wajen kasar Afrika ta kudu, Reginah Mhaule, ta bayyana hakan ne a lokacin da take gabatar da jawabi a wani taron karawa juna sani game da kungiyar BRICS a Afrika.

Mhaule tace, sun yarda cewa tasirin kungiyar a matakin kasa da kasa ya bada gudunmowa wajen kara bunkasa cigaban tattalin arziki da siyasar duniya. Kuma cigaban da aka cimma kawo yanzu ya samu ne sakamakon yin aiki cikin hadin gwiwa da kuma aiwatar da dukkannin yarjejeniyoyin da aka kulla wadanda a ko da yaushe ake kulla su bisa amincewar juna.

Tace kasar Afrika ta kudu ta shiga cikin BRICS ne domin kawo daidaito a harkokin kasa da kasa. Tace wadannan kasashen sun yi hadin gwiwa da juna ne bisa manufar kawo sauye sauye a tsarin duniya da nufin yin tasiri game da tsarin fada a ji a duniya, tattalin aziki, raya al'adun da kuma yanayin zamantakewar al'umma baki daya.

Kasar Afrika ta kudu ce zata karbi bakuncin taron kolin BRICS karo na 10 a wata mai zuwa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China