in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta jagoranci kasashen BRICS wajen farfado da tattalin arziki a nan gaba
2017-09-08 20:40:57 cri
Babban direktan cibiyar harkokin kimiyyar mulki ta kasa da kasa Sofiane Sahraoui ya bayyanawa wakilan kamfanin dillancin labaru na Xinhua a kwanakin baya cewa, makomar bunkasuwar kasashen BRICS a shekaru 10 masu zuwa ta dogara ga jagorancin kasar Sin a fannin bunkasuwar tattalin arziki.

Sahraoui ya bayyana cewa, halin rashin tabbas da ake fuskanta a duniya yanzu, ya kasance wata dama ga tsarin hadin gwiwar kasashen BRICS, kuma kungiyar BRICS za ta zama wata kungiya mai farfado da tattalin arziki da kwanciyar hankali a fannin siyasa.

Sahraoui ya kara da cewa, tsarin samun bunkasuwa na kasar Sin ya jawo hankalin kasashen duniya da dama, domin ba shi da wata alamar mulkin mallaka, kana ba ya tilastawa sauran kasashen duniya amfani da ra'ayinta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China