in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na son ba da taimako ga kasashe da yankuna masu fama da matsalar fashewar nakiyoyi
2018-06-30 16:30:35 cri
Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Wu Haitao ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da aiwatar da harkokin kasa da kasa yadda ya kamata, da kuma ba da taimako ga kasashe da yankunan da ke fama da matsalar fashewar nakiyoyi, tare da ba da gudummawa da hadin gwiwar gamayyar kasa da kasa wajen warware matsalar jin kai da tashin nakiyoyin da aka binne a karkashin kasa da sauran boma-bomai suka haddasa.

A yayin taro kan batun nakiyoyin da aka binne a karkashin kasa da kwamitin sulhu na MDD ya kira a jiya, Wu Haitao, ya bayyana cewa, a halin yanzu, akwai kasashe da dama dake fama da matsalar fashewar nakiyoyi, kuma yake-yake da tashe-tashen hankali da suka faru a wasu yankuna sun haifar da karin matsalolin tashin boma-bomai ga al'ummomin da abin ya shafa. Kuma, a shekarun baya bayan nan, 'yan ta'adda da masu tsattsauran ra'ayi sun ci gaba da yin amfani da boma-bomai masu saukin sarrafawa domin kai hare-hare.

A don haka ya ce, karfafa hadin gwiwar kasa da kasa ta fuskar warware matsalar nakiyoyi yana da muhimmiyar ma'ana wajen kiyaye tsaron al'ummomi da dukiyoyinsu, da tabbatar da gudanar aikin kiyaye zaman lafiya yadda ya kamata da kuma cimman burin neman dauwamammen ci gaba ya zuwa shekarar 2030.

Bugu da kari, Mr. Wu ya ce, kasar Sin ta ba da taimako wajen kawar da nakiyoyin da aka binne, ga kasashen Asiya da Latin Amurka sama da 40 ta hanyar samar musu na'urorin kawar da nakiyoyin da aka binne da kuma horar da ma'aikatansu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China