in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta aike da 'yan sadan wanzar da zaman lafiya zuwa Sudan ta kudu da Cyprus
2018-04-20 10:50:05 cri
Kasar Sin za ta tura 'yan sandan wanzar da zaman lafiya Sudan ta kudu da Cyprus, domin gudanar da aiki karkashin shirin wanzar da zaman lafiya na MDD.

A cewar ma'aikatar kula da tsaron al'umma ta kasar Sin, ayarin 'yan sandan mai mambobi 12 shi ne kashi na 17 da za a tura Sudan ta Kudu, inda za su kama hanya a ranar Lahadi mai zuwa.

Jami'an masu matsakaicin shekaru 37, sun fito ne daga bangarori daban-daban na rundunar 'yan sanda, kana sun kware kan harsunan kasashen waje.

Tun bayan shiga shirin wanzar da zaman lafiya na MDD a shekarar 2000, kasar Sin ta tura jimilar jami'an 'yan sanda 2,614 ga shirye-shiryen wanzar da zaman lafiya 9 da kuma hedkwatar MDD dake birnin New York. A cewar ma'aikatar, jami'an sun samu kyakkyawar shaida a fadin duniya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China