in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta ce wajibi ne shirye-shiryen wanzar da zaman lafiya su rika mutunta ikon kasa na mallakar yankunanta
2018-03-29 09:56:56 cri
Wakilin dindin-din na kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya ce dole ne shirye-shiryen kiyaye zaman lafiya na MDD su rika kiyaye dokokin majalisar tare da mutunta ikon da kasashen da suke aiki cikinsu ke da shi na mallakar yankunansu.

Ma Zhaoxu, ya bayyana haka ne a jiya, yayin wata muhawara na kwamitin sulhu na majalisar kan hada hannun wajen daukar matakin inganta ayyukan shirye shiryen wanzar da zaman lafiya.

Ya ce ya na da matukar muhimmanci a inganta karfin kasashen dake bada gudunmuwar soji, musammam kasashe masu tasowa, tare da kara inganta hadin kai da kungiyoyin shiyya.

Da yake jadadda matsayin kasar Sin, wadda ita ce ta 2 wajen bada gudunmuwar dakaru cikin mambobin kwamitin, kuma ta 2 wajen bada gudumuwa mai tsoka ga kasafin kudin shirin wanzar da zaman lafiya, ya ce kasar Sin ta kafa rundunar sojin mai dakaru 8,000 dake jiran ko ta kwana, kuma tuni ta tura kashin farko na jiragenta masu saukar ungulu zuwa nahiyar Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China