in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasashen waje sun isa birnin Qingdao don halartar taron kolin SCO
2018-06-09 20:06:02 cri
Ana gudanar da taron kolin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai karo na 18 a birnin Qingdao na lardin Shandong na kasar Sin tsakanin ranar 9 zuwa ranar 10 ga wata. Ya zuwa yammacin yau Asabar, dukkan shugabannin mambobin kungiyar da na kasashe 'yan kallo sun isa birnin Qingdao don halartar taron.

Shugabannin mambobin kungiyar da suka zo birnin Qingdao don halartar taron sun hada da: firaministan kasar Indiya Narendra Modi da shugaban kasar Kazakhstan Nursutan Nazarbaev da shugaban kasar Kyrgyzstan Sooronbay Zheenbekov da shugaban kasar Pakistan Mamnoon Hussain da shugaban Rasha Vladimir Putin, da na Tajikistan Emomali Rakhmonov, da kuma shugaban Uzbekistan Shavkat Mirziyoyev.

A sa'i daya kuma, shugabannin kasashe 'yan kallo wadanda suka zo sun hada da: shugaban kasar Afghanistan Ashraf Ghani da shugaban Belarus Alexandr Lukashenko da na Iran Hassan Rouhani da kuma shugaban kasar Mongoliya Khaltmaa Battulga.

Bugu da kari, wasu wakilan MDD da wakilan kungiyoyin kasa da kasa da abin ya shafa su ma za su halarci taron. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China