in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya gana da manyan jami'an tsaron kasashe mambobin SCO
2018-05-22 19:38:28 cri
Yau Talata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugabannin tawagogin wakilan kasashe mambobin kungiyar hadin kai ta Shanghai wato SCO a takaice a nan birnin Beijing, wadanda ke halartar taron sakatarorin tsaron kungiyar karo na 13 .

A yayin ganawar Xi ya nuna cewa, tun bayan da aka kafa kungiyar SCO, kullum kasashe mambobin suna ba da muhimmancin da batun tabbatar da tsaro da zaman lafiya.

Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da hada kai tare da kasashe mambobin kungiyar don kulla wata sabuwar dangantakar kasa da kasa bisa nuna girmama juna da adalci da samun nasara tare, don samun makomar bai daya ta dan Adam.

Wakilan tawagogin kasashen waje sun yi jawabi cewa, kasashensu na goyon bayan shawarar da kasar Sin ta gabatar a matsayinta na kasar dake shugabantar kungiyar a fannonin tabbatar da ra'ayin bai daya da shugabannin suka cimma, da tinkarar kalubalen da kasashe mambobin kungiyar ke fuskanta, da kiyaye zaman lafiya da tsaron kasa da kasa. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China