in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe 5 sun lashe zaben wakilan wucin gadin kwamitin sulhu na MDD
2018-06-09 16:21:47 cri
Babban taron zauren MDD ya zabi kasashen 5 da suka hada da Jamus da jamhuriyyar Dominican da Afirka ta Kudu da Belgium da Indonesia, a matsayin wakilan wucin gadi na kwamitin sulhu na MDD na shekarar 2019 da shekarar 2020.

Kasashe 6 ne suka shiga zaben na wannan karo da aka yi a jiya. Da yake an zabi wakilan wucin gadin ne bisa yankuna daban daban, shi ya sa, kasashen Jamus da jamhuriyyar Dominican da Afirka ta Kudu da Belgium ba su da abokan karawa, yayin da kasashen Indonesia da Maldives suka nemi wakilcin yankin Asiya da Pacific.

Babban taron zauren MDD, ya zabi wakilan wucin gadin kwamitin sulhun ne ta hanyar jefa kuri'un da babu suna, kuma kasashen da suka sami kuri'u sama da kashi 2 bisa 3 ne suka lashe zaben. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China