in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya bayyana damuwa game da halin da ake ciki a Mali
2018-06-03 15:12:31 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya bayyana damuwa game da rikicin da ya auku a Bamako, babban birnin Kasar Mali, wanda ya samo asali daga zanga-zangar da bangarorin adawa suka yi.

Sanarwar da kakakin Majalisar Farhan Haq ya fitar, ta ruwaito Antonio Guterres na kira ga dukkan bangarori su kwantar da hankali tare da kauracewa tada fitina, sannan ya bukaci 'yan siyasa da al'umma, su duba yuwar hawa teburin sulhu domin samun kyakkyawan yanayin gudanar da sahihin zabe mai adalci.

Sakatare Janar din ya bayyana takaici game da yadda gwamnati ta haramtawa bangarorin adawa gudanar da zanga-zanga. Ya ce abu ne mai muhimmanci a tattauna don samun maslaha game da rikicin siyasar kasar, yana mai kira ga Gwamnatin ta tabbatar da kare hakkokin dan Adam da 'yancin bayyana ra'ayi. (Fa'iza Msuatpha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China